YAR TALLAH Complete Hausa Novel




Tafe tAke tana rusa kuka wiwi,,,,,wiwi Duk ta hada miyau majina da hawaye ta dame fuska gaba daya Rungume take da tiren tallan tata wanda ba komai a cikinsa
sai ihu take kwararawa tana kiran wayyo kudina wayyo ni kudina .Mutane sai kallonta sukeyi masu tausayi daga cikinsu su kirata suji abinda ya faru su lallasheta ta tafi
A haka taita saqawa ta lunguna harta iso layin gidansu Tunda ta iso layin rabi,u wanda bai wuce dan kimanin shekara goma sha huduba kejiyo sautin kukanta yana duqe
yana faman wanke wanke Yai niyyar miqewa karaf sukai ido hudu da inna laure Ta watsa masa wani irin kallo simi simi ya koma yaci gaba da wanke wanken Tace munafuki dan iska wlh ka sake tashi baka gama wanke wankennaN ba saina karya maka qafafu Ta qara jan tsaki ta hankade labule ta shige Daki Rabi,u yai saurin tsame hannunsa daga wanke wanken ya Kwasa yai waje da gudu A bakin kofar zauren sukai kicibus yace waya tabakine saude?
Ta qara fashewa da wani kukan wanda yafi nada sauti
Rabiu ya qara janta jikinsa kiyi haquri saude fadamin meke
faruwa? Tadan sassauta da kukan tace kudina yaya kudin tallah na
wani ya kwaceminsu Rabiu ya dafe kirji ido waje yace garin yaya saude? Kinsan halin inna laure kuma dukanki zatayi Ta qara fashewa da kuka wayyo yaya dan allah ka roqeta karta dakeni
Ya danyi jimm kiyi haquri saude babu yaddah zan iya kixo muje kawai ta dakekin Ta qanqameshi wayyo yaya wlh yankani zatayi
Idanunsa suka kawo kwallah ya cije yace zo muje saude insha allahu bazata dokekiba kinji?

5 Comments

Previous Post Next Post

Post Ads 1

Post Ads 2

Advertising Space